Hukumar yaki da rashawa ta Nijeriya wato EFCC reshen dake kula da shiyyar Sakkwato, Zamfara da Kebbi ta baki shugabanta, Abdullahi Lawal, sun bayyana cewa; sun yi nasarar cafke Sakataren ilimi Ishaka Abdullahi, da mataimakinsa, Abdullahi Idris, da kuma ma’aji da mai tattara kudi Abdullahi Dadi da Idris Wambai na ma’aikatar ilimi na karamar hukumar Sabon Birni dake jihar Sakkwato.
A cewarsa sun yi wannan kamen ne sakamakon karar da wadansu Malaman makaranta har su 114 suka shigar gaban hukumar suna mai kalubalantar rashin biyansu albashi da ba a yi ba wata da watanni.
Shugaban ya ce; bayan wannan korafin sun gudanar da bincike inda suka gano bayanai masu yawan gaske wanda ya ba su damar cafke wadanda ake zargi cikin ma’aikatar ilimin.
Ya kara da cewa; tun shekarar 2013, karamar hukumar ta Sabon Birni ta bude wani asusun na daban na ma’aikatan bogi har 208. Ya ce; sun yi wannan nasarar ne ta hanyar rage albashin wasu da kin biya asalin ma’aikatan ana kuma biyan wadannan ma’aikatan boge.