A bisa kokarin shawo kan dukkanin matsalolin da suke yankin karamar hukumar Birnin Gwari, gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad el-Rufai, a jiya Asabar ne ya kaddamar da Rundunar sojin sama ta 271 da ke Birnin Gwari. Rundunar sojin sama ta ‘271 NAF’ dai shugaban sojojin saman Nijeriya (CAS) Air Marshal Sadik Baba Abubakar ne ya samar a bisa yunkurinsu na tabbatar da shawo kan matsalolin tsaro a wannan yankin. Ya kuma yaba wa sarkin Birnin Gwari, Alhaji Jibril Zubairu Maigwari II a bisa bayar da tallafin wani kaso na filin da aka gina wannan barikin sojin saman da alkawarin gwamnatin jihar za ta biya diyyar filin yadda ya dace. Gwamnan jihar Kadunan ya roki shugaban sojin saman da cewar su taimaka wajen samar da sashin Rundunar soji na musamman da zai ke aiki a babban titin Kaduna zuwa Abuja domin taimakawa wajen shawo kan matsalolin tsaro musamman na masu garkuwa da mutane da ‘yan fashi da makami. Ya kuma sake rokon cewar a kuma kara gina wani sabon Barikin sojin sama a karamar hukumar Kajuru da ke cikin jihar ta Kaduna. Ya bayar da tabbacin cewar shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tashi tsaye wajen kawo karshen matsalolin tsaro, “Dukkanin matsalolin tsaro daf suke da zama tarihi, jam’iyyar APC ta maida hankalinta wajen tabbatar da kowani dan Nijeriya ya yi alfahari da ita. “Matsalolin garkuwa da mutane da fashi da makami sun karu a kwanakin nan, amma muna godiya wa Allah jami’an tsaro musamman NAF sun tashi tsaye wajen inganta hidimar tsaro da shawo kan matsalolin nan ta hanyar daburu da hikimomi na kwarewa. “Kaddamar da wannan barikin sojin 271 da ke Birnin Gwari ya zo a daidan kan gabar da ta dace, wanda zai taimaka wa Operation DIRAN MIKIYA, da kuma Operation SHARAN DAJI da suke kokarin tabbatar da samar da zaman lafiya a wannan yankin,” A cewar shi. Da yake jawabinsa tun da farko, shugaban sojin sama ta Nijeriya CAS ya shaida cewar samar da barikin wata hanyace da suke kan bi wajen shawo kan matsalolin tsaro, ya ce sun maida hankalinsu wajen tabbatar da kawo zaman lafiya da magance matsalolin ‘yan ta’adda a Nijeriya.