Evans, wannnan shahararren mai garkuwa da mutane ya tsiyace ya kasa biyan tara Mai Shari’a Hakim Oshodi na kotun babbar kotu dake zaman ta a Ikeja ya bayar da umarni ga jami’an tsaro da su ci gaba da tsare shahararren mai garkuwa da mutanen nan Evans tunda ya kasa biyan tarar da shari’a ta yanke masa kan laifukan da yake aikatawa.
An yanke ma Evans hukuncin zaman gidan kaso a juma’a, Babban lauya mai kare Evans Moyosore Onigbanjo (SAN) ya sanar da kotu ta wayar tarho cewa wanda suke karewan bashi da kudin da zai biya abunda kotu ta yanke mishi.
Idan baku manta ba a ranar 30 ga watan Agustan shekarar 2017 ne Evans ya chaza lauyoyin dake kare shi, bayan nan ya sake chanzawa kusan sau uku.