Ƙungiyar masu gidajen biredi ta ƙasa reshen jihar Kano ta ce tilas ce ta sa ta yin ƙari a farashin burodi saboda tashin gwauron zabin da farashin kayan haɗinsa ya yi.
Rahotanni sun nuna cewa ƙarin farashin a jihar Kano ya fara aiki ne a ƙarshen mako kuma ya shafi dukkannin gidajen burodi a jihar.
“Gaskiya ne mun yi ƙari kuma ya fara aiki daga ranar Asabar. A zahirin gaskiya ana yin kasuwanci ne domin riba, kuma a cikin ‘yan watannin nan kawai an ƙara kimanin N4,000 a kan farashin kowane buhun fulawa”, cewar Sakataren ƙungiyar.
Sakataren ya ƙara da cewa, “Duk burodin N50, N60 zuwa N70 yanzu mun kara masa N10 a kan farashinsa na da.
“Na N100 zuwa N150 kuma yanzu mun kara masa N20, yayin da dukkan burodin N200 zuwa sama yanzu mun kara masa N50.
“Idan kuka yi la’akari za ku ga kusan dukkan kayan haɗa burodi kama daga fulawa zuwa sinadarin haɓaka ta, sukari zuwa sauran kayan haɗinsa komai farashinsa ya yi tashin gwauron zabi.
“Yawanci mutanenmu sun gwammace idan irin hakan ta faru mu rage ingancin burodin a maimakon mu ƙara farashi, hakan kuma ba shi da kyau ko kaɗan”, inji Malam Kabiru.
Daga nan kuma ƙungiyar ta yi kira ga al’umma da su karɓi ƙarin da zuciya ɗaya, tana mai cewa su ma ba da son ransu suka yi ƙarin ba.
To sai dai wani mai sana’ar sayar da shayi da biredi a unguwar Rimin Kebe da ke Kano Muhammadu Boss, ya ce ya zuwa safiyar ranar Litinin ba su ga ƙarin da aka ce an yi ba.
“Ka san a mafi yawan lokuta idan masu gidajen biredi za su yi ƙari yawanci abin da suke yi shi ne su rage ingancinsa a maimakon ƙara kuɗinsa.
“Na fi zaton abin da suka yi ke nan wannan karon ma, saboda an ce tun ran Asabar aka ƙara amma mu ba mu ga ƙarin ba,” inji Abdullahi.
A nasu ɓangaren kuwa, magidanta da kan sayi biredin domin karin kumallo sun koka kan cewa ƙarin zai shafe su matuƙa.