By Abbas Yakubu Yaura
Majalisar Dinkin Duniya ta jajanta wa gwamnati da al’ummar Saliyo kan fashewar wata tankar mai a birnin Freetown.
Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya António Guterres ya bi sahun daukacin tsarin Majalisar Dinkin Duniya a Saliyo don nuna alhini ga mutanen da hadarin tankar mai ya rutsa da su a daren Juma’a a babban birnin kasar.
Guterres, a wata sanarwa daya fitar, yace ya yi matukar bakin ciki da asarar rayuka da aka yi, sakamakon hatsarin, lokacin da motar dakon mai ta yi karo da wata babbar mota a wata mahadar cunkoson jama’a dake wajen birnin Wellington, inda ta zubar da mai, kafin ta kama da wuta.Gobarar data tashi ta cinye wasu motoci da masu tafiya a kusa da wurin.
“Babban sakataren ya mika ta’aziyyarsa ga jama’a da gwamnatin Saliyo tare da yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki cikin gaggawa.
“Majalisar Dinkin Duniya tace a shirye take ta ba da goyon bayan daya dace bayan faruwar wannan mummunan lamari,” in ji kakakinsa, Stéphane Dujarric.
Ofishin Majalisar Dinkin Duniya a Saliyo ya kuma fitar da wata sanarwa inda ya yi fatan samun kwanciyar hankali ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu, da gwamnati da al’ummar Saliyo, a cikin wannan lokaci na bakin ciki.
Kaxalika “Majalisar Dinkin Duniya tace za ta yi aiki tare da gwamnatin kasar don shawo kan abin da aka ce mataimakin shugaban kasar Mohamed Juldeh Jalloh, ya bayyana a matsayin” bala’i na kasa, bayan ya ziyarci wurin da hadarin ya afku.”
Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta wallafa a ranar Asabar cewa “tana tattara kayayyaki na musamman”.sannan “Muna aiki don tura kwararrun masu kula da marasa lafiya da suka kone. Za mu ba da ƙarin tallafi kamar yadda ake buƙata, a wannan mummunan lokaci ga al’ummar Saliyo.”
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Rahotanni sun ce akalla mutane 99 ne suka mutu yayin da wasu fiye da 100 suka jikkata a wannan bala’in.