By Abbas Yakubu Yaura
Shugaban kasar Laberiya, George Weah, ya aike da sakon ta’aziyya ga shugaban kasar Saliyo Julius Maada Bio da ‘yan kasarsa kan fashewar tankar mai da ta afku a ranar 5 ga watan Nuwamba a birnin Freetown na kasar Saliyo.
Weah ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da Jarlawah Tonpo, mataimakin ministan yada labarai na Laberiya ya fitar a ranar Lahadi.
Shugaban yace ya yi matukar bakin ciki da mummunan hasarar rayuka da aka samu sakamakon fashewar, inda ya bayyana hatsarin a matsayin babban abin takaici ga yankin.
A cewar sanarwar, motar tankar ta yi karo da wata mota a wani yanki mai cike da jama’a na birnin, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu da dama.
Weah ya yi kira ga ‘yan kasar Laberiya da ‘yan Afirka ta Yamma dasu yi addu’a tare da Saliyo a daidai lokacin da kasar ke cikin tashin hankali sakamakon irin wannan mummunan lamari ya afku.
A wani bangare na Sanarwar na cewa, “Shugaban ya kuma mika sakon ta’aziyya ga takwaransa, Shugaba Julius Maada Bio, gwamnati da al’ummar Saliyo, da iyalan wadanda suka mutu, da kuma duk wadanda hadarin ya rutsa da su.
“Weah ya bayar da cikakken goyon baya da taimako na Laberiya yayin da hukumomin Saliyo suka fara kokarin jinyar wadanda suka jikkata da kuma dawo da wadanda suka mutu.
Shugaban na Laberiya ya roki Allah Madaukakin Sarki daya jikan wadanda suka rasu tare da yi wa wadanda suka jikkata adu’a.”