Babban Lauyan Najeriya mai rajin kare haƙƙin ɗan Adam Femi Falana (SAN) zai ɗaukaka ƙara kan hukuncin kisa da wata kotun Musulunci ta yanke wa wani matashi da ya yi ɓatanci ga Manzon Allah (SAW) a Jihar Kano.
A ranar Alhamis ma’aikatar shari’a ta jihar Kano ta sanar da miƙawa wakilan Falana kundin hukuncin kisa ta hanyar rataya da babbar kotun Musuluncin a jihar ta yanke wa matashin wanda ta samu da laifin ɓatanci ga Manzon Allah a wata waƙa.
“Ɓangaren shari’a ya samu takardar wakilan Falana na neman bayanan hukuncin a ranar Talata kuma an miƙa masa a ranar Laraba”, inji kakakin ma’aikatar, Babajibo Ibrahim.
Ya ce lauyan na so ne ya ƙalubalanci hukuncin kotun Musuluncin mako guda kafin cikar wa’adin kwana 30 da kotun ta bayar na ɗaukaka ƙarar kafin zartar da hukuncin da ta yanke.
A ranar 10 ga Agusta ne kotun Musuluncin ta yanke wa Aminu Yahaya Sherif mai shekara 30 hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samun shi da yi ɓatanci ga Manzon Allah (SAW).
Hukuncin kotun ya sa wasu iƙirarin kare haƙƙi suka ce ya yi tsauri, yayin da galibin al’ummar Musulmi ke yabawa da cewa hakan shi ne abin da addini ya tanada kuma zai magance katoɓarar a nan gaba.
Gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya yi alƙawarin rattaba hannu cikin gaggawa a kan hukuncin kotun da zarar lokaci ya cika, muddin ba a ɗaukaka ƙara ba, ko kuma da zarar kotun ƙoli ta tabbatar da hukuncin.
Kotun ta ba wa matashin wanda ke tsare a kurkuku wa’adin kwana 30 ya ɗaukaka ƙara ko kuma a zartar masa da hukunci.