Jami’an tsaro a Sudan sun kashe karin mutum daya yayin zanga-zangar da dubban ‘yan kasar ke cigaba da yi ta adawa da juyin mulkin da sojoji suka yi a farkon makon da ya kare.
Likitoci sun ce mutumin na uku da aka kashe a birnin Omdurman yau Asabar, ya mutu ne sakamakon harbin bindiga a kirjinsa.
A halin yanzu wadanda suka mutu tun bayan barkewar zanga-zangar kin jinin gwamnatin sojojin Sudan a ranar Litinin ya karu zuwa mutane 12, yayin da wasu kimanin 170 suka jikkata.
Zanga-zangar ta zo ne kusan mako guda bayan da sojoji suka tsare shugabannin farar hula na Sudan a ranar Litinin da ta gabata, tare da rusa gwamnatin rikon kwaryar dake jagoranci, da kuma ayyana dokar ta baci, lamarin da ya janyowa sojojin Allah wadai daga kasashen duniya.
Duk da zubar da jinin da ake samu ne kuma masu shirya zanga-zangar suka sha alwashin jagorantar sake fitar mutane akalla miliyan 1, don nuna adawa da kwace madafun iko da sojoji ke yi, kwatankwacin zanga-zangar da ta kai ga hambarar da gwamnatin tsohon shugaba Omar al-Bashir a shekarar 2019.