Fusatattun mutane sun kashe wani Ɗan Fashi da Makami da yaƙi Tuba
Wani magidanci mai matsakaicin shekaru mai suna Loni ya gamu da ajalinsa a safiyar Lahadi a jihar Osun.
Ana zarginsa da satar babur a unguwar Ireti Ayo da ke Ilesa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Soludo ya sanya Dokar hana zirga-zirgar shanu da kafa a Anambra
Ƴan Acaɓa ne suka kama shi wucewa a cikin , bayan kama shi yana kokarin satar Babur.
Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta, ta bayyana cewa Loni ya kwace babur din daga hannun wani mai babur a yankin, da yammacin ranar Asabar.
Majiyar ta bayyana cewa wanda ake zargin yana da bayanan fashi a baya ga ’yan sanda a Ilesa, ta bayyana cewa wasu ’yan kasuwar da suka gano barawo ne kuma suna sane da babur dinsa na kwace tarihi, suka tafi da shi suka kashe shi.
Ya kuma bayyana cewa rundunar ‘yan sandan Najeriya, A Division, Ayeso, Ilesa na sane da faruwar lamarin kuma an ajiye gawar tasa a dakin ajiye gawa na garin Ilesa.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Osun, Yemisi Opalola da aka tuntubi dan tabbatar da faruwar lamarin bai mayar da martani ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.