Wata kotun Majistiri dake zamanta a Abeokuta ta yankewa wani matashi mai suna Musa Anifowose dan shekaru 21 a duniya, hukuncin zaman gidan kaso na tsawon shekaru biyu bayan da aka same shi da laifin yi wa wata yarinya mai shekaru 8 fyade.
Mai Shari’a I.O Abudu tace dukkanin hujjojin da aka gabatar a gaban kotun sun tabbatar da cewa wanda ake zargin ya aikata laifin, dan haka ta yanke masa hukuncin shekaru 2 a gidan kaso.
Kuma ta kara da cewa mai laifin zai yi zamansa a gidan gyaran hali dake Oba.
https://dimokuradiyya.com.ng/6335-2/
Lauyan wanda suka shigar da karar ya bayyanawa kotu yadda matashin ya dauki yarinyar zuwa wani kangon wanda a nan ne ya aikata mata fyaden ba tare da kowa ya sani ba.
“Bayan ta koma gida ne mahaifiyarta ta lura da jini a jikinta, bayan da ta yi bincike sai ta gano cewa fyade aka mata”.
Laifin nasa dai ya sabawa kudin kare hakkin kananan yara karkashin sashi na 33 na jihar Ogun.