Gwamnan jihar Edo Mista Godwin Obaseki, ya bawa jami’an tsaro umarnin yin cikakken bincike domin gano wanda suka kashe Vera Uwaila Omozuwa, daliba ‘yar aji daya a Jami’ar Benin dake babban birnin jihar.
Ana zargin Omozuwa an mata fyade ne tare da fasa mata kai da abin kashe gobara a wajen bauta na Pentecostal.
A cikin wani jawabi da ya fitar, mai baiwa gwamnan shawara akan kafar yada labarai Mista Crusoe Osagie, yace gwamna Obaseki ya bawa hukumar’yan sanda umarnin yin bincike don gano wanda suka aikata laifin domin hukunta su.
https://dimokuradiyya.com.ng/fyade-yan-sanda-sun-kama-mutane-11-da-laifin-fyade/
“Mai girma gwamna ya nuna damuwarsa tare da jimamin rasuwar Omozuwa, kuma muna ci gaba sa tattaunawa da hukumar ‘yan sanda domin kamo duk wanda yake sa hannu wajen aikata wannan danyan aiki, domin girbar abinda ya shuka”.
Mista Osagie, ya kara da cewa gwamnan ya jajantawa iyayen mamaciyar tare da nuna alhininsa.
Yace tabbas dole a jajantawa iyayenta domin suna cikin mawuyacin hali na rashin ‘yarsu.