Hukumar ‘yan sanda a jihar Oyo ta bayyana nasarar cafko wani mutum da ake zargin yi wa wata mai ciki, Azeezat Somuyiwa fyade tare da kasheta a ranar 5 ga watan Yuni a jihar Oyo.
Rahotanni sun bayyana cewa an kashe matar ne da dutse bayan yi mata fyade a gidanta dake Aba Ijefun a karamar hukumar Akinyele jihar.
https://dimokuradiyya.com.ng/fyade-wata-ta-rasa-ranta-ta-hanyar-fyade/
Kakakin hukumar ‘yan sandan jihar Olugbenga Fadeyi, ya bayyana cewa “mun kama wani wanda ake zargin yana da sa hannu a kisan nata”.
Ya kara da cewa mai laifin yana basu bayanan da zasu taimaka musu wajen samun nasarar sake cafko wasu dake da hannu.