Wakilinmu Muhammad Gambo Damaturu
La’akari da irin matsalolin da ake fuskanta a harkar saida magani wanda hakan ke kawo yawaitar shaye-shaye, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya karfafa shirin yakan matsalar a jihar Kano.
Hakan ya sa Gwamnatin jihar ta warewa masu saida magani a jihar waje na musamman a unguwar Dangwauro dake cikin karamar hukumar Kumbotso.
Yace ware musu kasuwa ta musamman shine zai bada damar a kula da saida maganin tare da dakile yaduwar miyagun kwayoyi da yawaitar shaye-shaye tsakanin al’uma.
Wata sanarwa da ta fito daga ofishin skataren watsa labarai na Gwamna Ganduje, Abba Anwar, ranar Alhamis 25 ga watan Yuli 2019, tayi nuni da cewa hukumomi dake da alhakin kulawa da ababen ci da sha Kamar irin su NDLEA, NAFDAC, hukumar ‘yan sanda da dai sauran su, zasu samu saukin saka idanu akan shige da ficen magunguna.
Ganduje ya kara da cewa Gwamnatin sa tana kokarin inganta lafiyar al’ummarta ne yasa ta samar da wannan sabon tsarin.
Bayan jan hankalin da Ganduje yayiwa ‘yan kasuwan cewa su bada hadin kai yayin da Gwamnati ta bukaci da su koma sabuwar kasuwar da za’a gina musu, ya bada tabbacin cewa aikin sashe na farko a gina kasuwar zai soma ne a watan Disamba mai zuwa na shekarar 2019.