Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya shelanta bayar da ilimi Kyauta ga nakasassun da ke cikin Jihar a dukkannin matakai.
Da yake jawabi a bikin karban mulkin Jihar a ranar Laraba, 29 ga watan Mayu, Ganduje ya yi alkawarin bayar da ilimi kyauta ga dukkanin yaran Jihar da suka isa shiga makaranta.
Ganduje ya bayyana cewa, za kuma a yi rangwame sosai ga ‘yan asalin Jihar da suke cikin manyan makarantun Jihar, ya kara da cewa, gwamnatin na shi za ta yi amfani da nasarorin da ta samu a zangonta na farko a sassan ilimi, noma, manyan ayyuka da kuma sashen lafiya.
Ya ce, zangon mulkin na shi na biyu zai samar da wata sabuwar hukuma mai suna, Kano State Small Town Water Supply Agency, wacce za ta kula da samar da ruwa ga al’ummomin da suke a karkara.
Gwamnan kuma ya yi alkawarin habaka noma a Jihar, yana mai karfafa daukaka matsayin kananan manoma.
Ganduje ya sabunta aniyarsa ta yakar cin hanci da rashawa, ya kara da cewa, zangon mulkin na shi na biyu zai tabbatar da farfado da hukumar hana cin hanci da karbar rashawa ta Jihar ta yanda za ta yi aikinta sosai.
Ya kuma yi alkawarin gudanar da gwamnatin da za ta kunshi kowa da kowa ba tare da nuna bambancin jam’iyya ba, ya yi nuni da cewa, zamanin siyasa kuma ai ya wuce.