Gwamanan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa gwamnatin zata mayar da karatun firamare kyauta a jihar, tare da daukewa dukkanin masu bukata ta musamman nauyin kudaden makaranta na kowanne mataki.
A jawabin da gwamnan yayi jim kadan bayan shugaban jami’ar jihar, Mai shari’a Nuradeen Sagir Umar, tare da mataimakin shi, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, ya alkauranta mayar da kokarin wajen tilastawa yara zuwa makaranta tare da saukake musu biyan kudin makarantar Firamare.
Gwamnan yace, gwamnatin zata duba wajen saukaka kudaden da daliban makarantun gaba da sakandire suke biya. Ya kuma ce zasu kara hubbasa wajen inganta fannin lafiya a jihar.
Ganduje dai yace gwamnatin ta shirya yakar matsalar rashin ruwa a jihar, ya ce gwamnatin zata kirkiri sabon kamfanin mai suna “Kano State Small Town Water Supply Agency” domin samar da ruwa a cikin kauyukan jihar ta Kano.