Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje yayi afuwa ga daurarrun gidan gyaran hali 90 a nan Kano ciki kuwa har da musu hukuncin Kisa.
Dr Abdullahi Umar Ganduje ya amince da sakin nasu ne yau Asabar bayan da ya ziyarci gidan gyaran halin dake Kano.
Kakakin hukumar kula da gidajen gyaran hali na jihar Kano DSC Musbahu Lawan K Nassarawa ne ya bayyana hakan ga a wata sanarwa da ya aikowa da jaridar Dimokuradiyya, a yammacin ranar Asabar.
Kontrolan hukumar gidajane gyaran hali na jihar Kano Sulaiman M Inuwa ya yaba da wannan yunkuri na gwamnatin Kano, tare kuma da yabawa irin gudunmawar da gwamanan Kano ke bawa hukumar wajen gudanar da aiyukansu.
Yayin ziyarar gwamna Ganduje ya bada tallafin shanu, raguna da kuma kayan abinci domin yin bikin sallah a gidajen gyaran halin.
Kazalika gwamnan ya kuma raba musu kudi naira dubu biyar, don suyi kudin mota tare da bukatar su zama mutanan kirki anan gaba.