Za a ci gaba da gasar Jamus ta Bundesliga ranar Asabar 16 ga watan Mayu ba tare da ‘yan kallo ba, domin a karkare kakar 2019-20.
Hakan zai sa gasar za ta zama ta farko a nahiyar Turai da za a ci gaba da buga kwallon kafa, tun bayan da cutar korona ta haddasa tsaiko.
Cikin wasannin farko da za a yi ranar Asabar har da na hamayya tsakanin Schalke da Borussia Dortmund.
Mai rike da kofin bara, Bayern Munich, wadda ke mataki na daya a kan teburin bana da tazarar maki hudu za ta ziyarci Berling ranar Lahadi.
Sauran wasa 11 a kammala kakar shekarar nan, kuma tsakanin 27 zuwa 28 ake sa ran buga wasannin makon karshe a gasar ta Bundesliga ta bana.
Hukumar kwallon kafar Jamus ta ce za a koma wasannin ne. bayan da aka cimma yarjejeniyar kula da lafiya, kuma babu ‘yan kallo, sannan za a yi wa ‘yan kwallo gwajin cutar korona.
Mutum 300 da ya hada da ‘yan wasa da jami’ai da ma’aikata aka sa ran su kasance a cikin fili a lokacin da ake gudanar da wasannin.
Ranar 13 ga watan Maris aka dakatar da dukkan wasannin kwallon kafa a Jamus don gudun yada cutar korona, yayin da ‘yan wasa suka koma yin atisaye a tsakiyar Afirilu tare da matakan hana yada annobar.
Ga jadawalin wasannin da za a buga
Ranar Asabar
Augsburg da Wolfsburg
Borussia Dortmund da Schalke
Eintracht Frankfurt da Borussia Monchengladbach
Fortuna Dusseldorf da Paderborn
Hoffenheim da Hertha Berlin
RB Leipzig da Freiburg
Ranar Lahadi
Cologne da Mainz
Union Berlin da Bayern Munich
Monday
Werder Bremen da Bayer Leverkusen
Daga Bbc Hausa