Rahotanni daga jihar Kaduna na nuni da cewa; sama da gidaje 100 ne suka amfana da kayayyakin abinci da gwamnatin jihar tare da hadin guiwar kungiyoyin da ba na gwamnati ba suka raba.
Rabon abincin ya gudana ne a karkashin kulawar ma’aikatar tallafawa al’umma tare da gidauniyyar ‘Muzaif Foundation’ da kuma ‘Gracious Givers Foundation,’ a wani mataki na taimakon al’umma.
Kwamishiniyar Tallafawa al’umma ta jihar, Hajia Hafsa Baba, ta ce sun bada tallafin ne a wani yunkuri na ma’iakatar wajen taimakon marasa galihu a daidai wannan lokaci da ake fama da annobar cutar korona.
Kwamishiniyar, wanda Zahida Jibril, Babbar Jami’ar Gidauniyyar ‘Muzaif Foundation’ ta wakilce ta, ta kara da cewa; ma’aikatar za ta ci gaba da taimakon marasa galihun a jihar a wani mataki na rage wa marasa shi radadin talauci.
Shima shugaban Gidauniyyar ‘Gracious Foundation’, Aminu Bashir ya ce marasa galihu suna da matukar bukatar taimako a daidai wannan lokaci. Ya yi kira ga kungiyoyi da su rika bayar da irin wannan tallafin ga marasa shi.
Malam Usaini Ahmad, daya daga cikin wadanda suka amfana da wannan tallafin ya mika godiyarsa bisa wannan, inda ya ce ba su taba samun irin wannan tallafin ba a baya.
Kayayyakin abincin da aka raba ya hada da shinkafa, gari, semovita, inda al’ummar yankin Nasarawa dake Kaduna suka amfana da wannan tallafin.