Gidauniyata bata taɓa Tilasta Kiristoci su karɓi Musulunci Ba — Martanin Ganduje Ga Babachir
Gwamnan Jahar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya Musanta kalaman tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya Babachir Lawal cewa Gidauniyar Ganduje ana amfani da’ita domin tilasta Kiristoci shiga Musulunci.
A lokacin da yake nuna ƙin amincewar sa ga Sanata Kashim Shettima a matsayin abokin takarar Bola Tinubu Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a Jam’iyyar APC, Lawal ya ƙalubalanci Ganduje na yunƙurin musuluntar da Najeriya.
KARANTA WANNAN LABARIN:;NMA ta buƙaci Adalci ga ƴan uwan Majinyacin da suka Jikkata Likita
Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayyar yace Gidauniyar an kirkire ta da manufar Tilasta Kiristoci karɓar Musulunci.
Amma a cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labaru Malam Muhammad Garba ya fitar a madadin Ganduje, yace wannan Kalamai ƙarya ce tsantsagwaron ta.
Yace Musulunci yana ba kowa dama ya zaɓi Addinin da yake so, ya na baiwa Waɗanda ba musulmai ba dama ta bangaren tattalin arziki, Al’ada da Shuwagabanci.
Yace ba’a taɓa samun wani Kirista an tilasta shi karɓar Musulunci ba, domin tana akan koyarwar musulunci.