Hukumar gudanarwar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Gombe United ta bayyana cewar awannan rana ta Juma’a 18 ga watan Satumba na shekarar 2020 zata yiwa ‘yan wasan ƙungiyar gwajin lafiya na cutar nan ta Coronavirus data gallazawa duniya.
Shidai wannan gwajin cuta ga dukkanin ‘yan wasan da suke fafata gasar ajin Firimiya ta ƙasar nan da kuma ‘yan wasan da suke fafata gasa mai daraja ta biyu wato National League da masu horas dasu duk wajibi ne sai anyimusu kafin a dawo atisaye domin tunkarar sabuwar kakar wasa daza a shiga ta 2020 zuwa 2021.
Za a fara wannan gwajin a wannan rana ta Juma’a da misalin ƙarge 9:30 zuwa a wajen katafaren saukar baƙi na A.Y Guest House kusa da Dukku Motor Park dake jahar ta Gimbe a cewar shugaban ƙungiyar ƙwallon ƙafan ta Gombe United wato Dr. Larry Daniel.
Gombe United dai a wannan kakar wasan ba gasar ajin Firimiya ta ƙasar nan zata fafata ba, inda zata fafata a gasa mai daraja ta biyu wato gasar ajin ƙwararru ta ƙasar nan.
Daga ƙarshe Larry ya bayyana cewar duk ɗanwasan da aka kama da laifin ƙin zuwa a yimasa gwaji ba to ya ƙaddara a ransa cewar shi ba ɗan wasan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Gombe United bane kawai yaje ya nemi wata ƙungiyar.