A cikin wata sanarwa da gwamnatin Ghana ta fitar ta hannun ministan yaɗa labaranta Kojo Nkrumah a ranar Lahadi, gwamnatin Ghana ta musanta dukkan zarge-zargen kuma ta ce bata ji dadin kalaman da ministan harkokin yaɗa labaran Najeriya ya yi kan dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.
Al’amarin ya samo asali ne da aka rushewa Najeriya ofishin jakadancinta dake ƙasar ta Ghana, wanda hukumar ƙasar gwamnatin Najeriya ta karɓi hayar filin ne a wajen wani mutum.
A cewarsa, yarjejeiyar da suka sa wa hannu ta ƙare aiki tun shekara 46 da suka gabata ba tare da Najeriya ta sabunta yarjejeniyar ba.
Nkrumah ya kuma ƙaryata zargin da Najeriya ta yi na rushe wani gini mallakar ofishin jakadancin da ke lamba ta 19/21 layin Nyerere Street a birnin Accra. Ya ce ba gwamnatin Ghana ce ta rushe ginin ba amma kuma gwamnatin ta ɗauki nauyin sake gina ginin da aka rushe domin hana taɓarbarewar dangantaka tsakaninta da Najeriya.
Sai dai a baya-bayan nan ne Ministan yaɗa labarai na Najeriya Mista Lai Mohammed ya shaidawa manema labarai cewa ƙasar ta Ghana ta kwaso ‘yan asalin ƙasar nan guda 825 kuma suka dawo da su Najeriya daga tsakanin shekara ta 2017 zuwa 2019.
Gwamnatin ƙasar Ghana ta kuma yi magana kan zargin rufe shagunan ‘yan Najeriya a shekarar 2019 zuwa 2020, ta ce bayan da gwamnati ta gano akwai rashin bin ƙa’idojin kasuwanci daga dukkan ‘yan ƙasa da baƙi, ta yi ƙoƙarin tattaunawa da su da basu shawarar cika ƙa’idojin amma suka yi burus.
A cewarsa, haka ne ya sa doka ta yi aikinta. Sai dai sanarwar ta ce ministan masana’antu ya sa baki aka buɗe shagunan da aka rufe tare da basu lokaci domin cika sharuɗan.
Sanarwar ta ce a halin yanzu, babu wani shagon ɗan Najeriya da yake rufe a Ghana.