Gwamna Oluwarotimi Akeredolu na jihar Ondo ya bukaci gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Mista Godwin Emefiele, da ya yi murabus idan yana da sha’awar tsayawa takarar shugabancin kasa a 2023.
Akeredolu ya yi wannan kiran ne sa’o’i bayan da gwamnan CBN ya shiga takarar shugaban kasa a zaben 2023 mai zuwa.
Emefiele ya karbi fom din Naira miliyan 100 daga hannun sakataren jam’iyyar a dakin taro na (ICC) da ke Abuja, a safiyar Juma’a.
Akeredolu, a wata sanarwa da ya sanyawa hannu da kansa, ya bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya soke nadin nasa, idan ya ki yin murabus, yana mai cewa, “Wannan wasa ne da aikinsa.”
“An yi ta yada jita-jita game da ayyukan bangaranci na karkashin kasa da ke da nasaba da shi ta wadannan halaye masu duhu a cikin ‘yan makonnin nan,” cewar gwamnan.
An kuma yada hotunan motocin da aka yi wa lakabi da aka siya don yakin neman zabe, a shafukan sada zumunta.
Matakin da gwamnan CBN ya dauka na tsayawa takarar shugaban kasa ya biyo bayan cece-kucen da aka yi na tsawon watanni da suka gabata dangane da muradin siyasar yankin Agbor, haifaffen jihar Delta, tsohon manajan daraktan bankin Zenith.
Da yake mayar da martani ga yunkurin neman kujera ta daya a Najeriya, ya bukaci masu hasashe da kada su dauke masa hankali, yana mai cewa gara ya mayar da hankali wajen daidaita manufofin kudin Najeriya da daidaita su da manufofin gwamnatin tarayya.