Gwamnan Jihar Bauchi Bala Abdulkadir Mohammed ya ayyana sabuwar kwamitin mutum goma sha uku don gano abin da ya haddasa rikici tsakanin manoma fulani Makiyaya a kauyen Zadawa dake karamar hukumar Misau na jihar Bauchi.
A yayin jawabin nasa ga manema labarai jim kadan bayan nada komitin Bincike na gaggawa a Dakin taro na Gidan Gwamnatin jihar Bauchi , ya nada kwamiti mai mutum 13 karkashin Air kwamanda Tijjani Baba Gamawa Domin bincike da gano Hakika in abinda ya faru Gwamnan ya basu makonni uku. Su Gabatar da rihoto kan Lamarin.
Gwamnan yace an kafa komitin ne Domin gano Bakin zaren rikicin da kuma warware shi Domin kauce ma sake faruwan haka a gaba.
Bugu da kari a gefe guda kuma Gwamnan Ya umarci Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Bauchi da ya yi amfani da rukunin tafi-da-gidanka na Jami’an tsaro Domin daidai Lamura a karamar hukumar ta Misau.
Sannan Gwamna Bala Mohammed ya kuma ba da sanarwar dakatar da Shugaban riko na karamar Hukumar ta Misau tare da mataimakinsa da wasu jami’an sa kai tsaye har zuwa lokacin da Za’a kammala bincike kan Lamarin
Rikicin dai na Misau ya haifar da asarar rayuka 9 da raunuka da yawa.
Bala Abdulkadir yayi kira ga jama’ar yankin da su kasance masu bin doka da oda, ya bada tabbacin cewa, duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci fushin doka.
A karshe Gwamnan yace a madadin gwamnati da mutanen jihar Bauchi Baki daya muna jajantawa ma ma Al’ummar Karamar Hukumar Misau kuma muna mika Sakon Ta’aziya ga iyalan wadanda suka rasu sakamakon rikicin .