By Abbas Yakubu Yaura
Gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi, a ranar Asabar din da ta gabata, ya bayyana rashin jin dadinsa game da ware hanyoyin gwamnatin tarayya a jihar daga cikin jerin hanyoyin da za a sake ginawa da kuma gyara su a karkashin kasafin kudin gwamnatin tarayya na shekarar 2022.
Bello ya bayyana rashin jin dadin nasa ne a lokacin da yake amsa tambayoyi a yayin taron manema labarai da aka gudanar a gidan gwamnati karo na 29 a Lokoja, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya ruwaito.
Gwamnan ya koka kan dalilin da ya sa aka rika daukar hanyoyin gwamnatin tarayya a jihar a matsayin wadanda ba su da karfin tattalin arziki duk kuwa da tsarin da jihar ke da shi.sannan Gwamnan ya kuma yi Allah wadai da rashin jajircewa wajen farfado da kamfanin karafa na Ajaokuta.
Sannan yayi gargadi game da barnar da akeyi da gangan, Ya kara da cewa hanyar Abuja zuwa Lokoja kadai tana da tsari, amma an ki kammala aikin tun gwamnatin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa gwamnan ya ziyarci ministan ayyuka da gidaje, Mista Babatunde Fashola, sau da dama, domin jawo hankulan ma hukunta kan hanyoyin gwamnatin tarayya a jihar Kogi, wadanda su ne jigon ci gaban tattalin arzikin kasar.
Tun da farko, shugaban kungiyar NMMA BoT, Dakta Haroun Adamu, ya bayyana cewa makasudin gudanar da taron shi ne a lissafta nasarorin da NMMA ta samu tsawon shekarun da sukayi da kuma karfafa su.Babban mai magana da yawun Farfesa Umar Pate ya gabatar da jawabi mai taken “Kafofin yada labarai da kalubalen gina kasa”
Pate, wanda shi ne mataimakin shugaban jami’ar tarayya da ke Kashere a jihar Gombe, ya bukaci ‘yan Najeriya musamman masu rike da mukamai da su yi kokarin tabbatar da hadin kan kasa.