Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe ya amince da Nair 422,179,194.07 a matsayin kudin fansho da giratuti ga ma’aikatan kananan hukumomi guda 359, da suka fito daga kananan hukumomi 17 na jihar.
Yarjejeniyar na nufin biyan kashi na 44 na ma’aikata da suka yi ritaya, wanda aka amince da su don sasantawa tsakanin Gwamnatin jihar iyalan ma’aikata 89 da suka mutu, da adadins kudin su ya Kai na naira 125, 264,991.02 da kuma guda 270 da suka yi ritaya, Kuma kudin su ya kai Naira 296, 914,203. 05.
A cewar wata sanarwa da mai taimaka wa gwamnan kan harkokin yada labarai, Mamman Mohammed ya fitar, ofishin babban mai binciken kudi na karamar hukumar ya tantance wadanda za su ci gajiyar shirin, domin tabbatar da biyan wadanda suka cancanta ne kawai.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yan sanda sun Ankarar da Al’umar Benue Kan Wasu Mahara
Idan za’a iya tuna ko a watan Fabrairun bana, Buni ya biya Naira miliyan 454.2 a matsayin tallafi ga ma’aikatan kananan hukumomi 276 da suka yi ritaya, da kuma 88 da suka rasu.
A wani Labarin Kuma na daban.
Gwamna Babagana Zulum na jihar Borno ya nada Bala Isa a matsayin sabon babban sakataren hukumar bayar da tallafin karatu ta jihar Borno.
Mai baiwa gwamnan shawara na musamman kan hulda da jama’a Isa Gusau shine Wanda ya bayyana hakan acikin wata sanarwa daya fitar ranar Litinin a Maiduguri,sannan kafin nadin Isa ya kasance malami a jami’ar jihar Borno.
Isa wanda ya kasance dan shekara hamsin ya fito ne daga karamar hukumar Bayo ta jihar Borno.sannan “Ya kuma kasance Babban Malami a Kwalejin Ilimi ta Kashim Ibrahim, dake Maiduguri.
“Isa, a halin yanzu yana kammala karatun digirinsa na uku a Jami’ar Maiduguri, inda yayi M.Sc.a fannin ilimin sinadarai, da kuma B.Sc. a dai wannan fanni, duka daga Jami’ar ta Maiduguri.
Sannan “Ya kuma yi Difloma a fannin Ilimi daga kwakejin ilimi ta Kashim Ibrahim dake Maiduguri.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa “Ya yi karatunsa na Sakandare a Makarantar Sakandaren Kimiyya ta Gwamnati dake Biu, da Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Kwaya Kusar.