Daga: Abbas Yakubu Yaura
Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya kaddamar da kwamitin fadakar da jama’a da dabarun mayar da martani domin dakile yawaitar hare-hare a kudancin jihar.
Ya kaddamar da kwamatin ne a garin Kafanchan a wani taro na garin kan shigar jama’a da kuma hada kan masu ruwa da tsaki domin dorewar huldar aiki, wanda mahukuntan karamar hukumar Kafanchan ta kira.
KARANTA WANNAN LABARIN: https://dimokuradiyya.com.ng/hari-kan-ayari-shugaban-kasa-samar-da-yan-sandan-jihohi-ne-kawai-mafita-akeredolu/
Gwamnan wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jiha Alhaji Balarabe Abbas ya ce kundin tsarin mulkin na daga cikin shawarwarin masu ruwa da tsaki na shiyyar bayan gudanar da ayyukan tsaro.
Ya kara da cewa kwamitin zai dauki nauyin dakile duk wata barazana ta tsaro ta hanyar gargadin jama’a da wuri da kuma kai rahoto ga jami’an tsaro.
Tun da farko, kwamishiniyar hukumar ta Kafanchan, Misis Phoebe Yayi, ta bukaci kwamitin da ya gudanar da aikin da himma domin tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a yankin.
Kwamitin mai mambobi 195 ya kunshi wakilai daga masarautu 13 a fadin kananan hukumomi uku na Jema’a, Kaura da Zangon Kataf.
A Wani Labarin Kuma An buƙaci Babbar Kotun Tarayya ta Abuja data hana Jam’iyyar APC daga musanya Alhaji Kabiru Masari a matsayin abokin takarar Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a Shekarar 2023, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
Bayan Tinubu ya zama Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a Jam’iyyar APC, ya mika sunan Masari ga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta INEC a matsayin wanda zai riƙe ofishin kafin samo wanda ya cancanta.
Amma wasu Jiga-Jigai a Jam’iyyar APC Wanda Suka kasance Deliget ne a Zaben Jam’iyyar na Shugaban Ƙasa, Zakari Maigari, da Zubainatu Mohammed sun je Kotu domin ta hana INEC daga amsar canja suna Mataimaki a Takarar Shugaban Ƙasa a Jam’iyyar APC, baya ga Masari.
Jam’iyyar APC, Tinubu, da Kabiru Masari sun kasance a matsayin wanda ake ƙarar a wata Shari’a mai lamba ta FHC/ABJ CS/1059/2022, Mai Kwanan watan r ga watan Juli na Shekarar 2022.
Wanda suke shigar da ƙara ta hanyar lauyan su Hakeem Kareem, suna so Kotu ta duba sashe na 142(1) d sashe na 29(1), 31, da 33 na Dokar Zaɓe, a Shari’an ce za’a iya korar abokin Takara, ko kuma canja shi da wani domin tunkarar Babban Zaɓe na Shekarar 2023.
Daga abinda suke so shine Kotu ta duba yiwuwar abinda tikiti ya bada na sashe 142(1) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, ya nuna cewa baza’a iya kai tsaye a kori Ɗan Takarar a Shugaban Ƙasa, idan aka duba Babban Zaɓen Shekarar 2003.