Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna a ranar Litinin a Kaduna ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa ‘yan uwansu a harin da ‘yan bindiga suka kai ranar Lahadi a kananan hukumomin Chikun da Igabi.
Ta’aziyyar na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaron cikin gida da harkokin cikin gida, Mista Samuel Aruwan ya fitar.
Aruwan ya ce jami’an tsaro sun bayar da rahoton cewa ‘yan bindiga sun kai hari a Kakkau Daji a karamar hukumar Chikun inda aka kashe wani mai ibada tare da yin garkuwa da wasu mutane da ba a tantance adadinsu ba.
Kwamishinan ya ce ‘yan bindiga sun kashe mutum daya a yankin Kangon Kadi da ke karamar hukumar Chikun, da kuma wani mutum daya a Barebari a karamar hukumar Igabi.
Ya ce ‘yan bindigar sun kuma kashe mutane biyu a yankin Sauran Giwa a lokacin da suke dawowa daga wurin ibada.
Aruwan ya kara da cewa El-Rufai ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda aka kashe a harin, ya kuma bukaci jami’an tsaro da su kara zage damtse wajen ganin an ceto rayuka da dukiyoyi a jihar.