• Gwamna Ganduje ya sanya hannu da wata kamfanin da zatayi aikin gida gidajen Malamai guda dubu biyar a jihar Kano.
• ya Kuma tsawaita shekarun yin ritayan daga 60 zuwa 65 na shekarun hai huwa, inda shekarun aiki kuwa zai tashi daga shekara 35 zuwa 40.
• Tun shekarar 2015 gwamnatin jihar Kano bata ta ba yin kasa a gwaiwa ba wurin biyan hukumar UBEC kudade domin inganta ilimi.
Biyo bayan ai’yana ilimi kwauta da kuma inganta wal-walar Malamai da ma’aikata, gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya sanya hannu kan kudurin gina gidajen Malamai guda dubu biyar a jihar.
Kwamishinan shari’a na jihar Mohammed Lawan ne ya sanya wa aikin hannu a madadin Gwamna Ganduje, wanda kuma Baban Daractan Kamfanin da zai yi aikin, Femi Adewole ya sanya hannu a madadin kamfanin.
KARANTA WANNAN LABARIN: Kwalara ta kashe mutun 7 a Abuja
A lokacin da ya ke jawabi a wurin taron da ya gudana yau Alhamis a Abuja, Ganduje ya ce, gwamnatin sa na iya Bakin kokarin ta, na dawo da Martaban ilimi a jihar.
Inda ya Kara da cewa, gwamnatin jihar ta tsawaita shekarun yin ritayan daga 60 zuwa 65 na shekarun hai huwa, inda shekarun aiki, zai tashi daga 35 zuwa 40.
Ya kara da cewa, lokacin da yanke hukuncin mai da ilimin furamari da na sakandare, kyauta Kuma tilas a jihar, kudurin shi, shi ne, ya kasance mara sa karfi sun sami ilimi.
A cewar sa, tun shekarar 2015, Gwamnatin Kano bata taba kazawa ba, , wurin bai wa hukumar kula da ilimi a matakin farko (UBEC) kudade.
Comments 1