Gwamnan jihar Zamfara, Bello Mohammed Matawalle ya ayyana mako mai zuwa daga Litinin zuwa Juma’a, (20 ga Yuni zuwa 24 ga Yuni, 2022) a matsayin makon da ba aiki don baiwa jama’a da ma’aikatan jihar damar zuwa yankunansu da kuma karbar katin zabe na dindindin, (PVC).
Gwamnan ya umurci dukkanin kwamishinonin da masu ba da shawara na musamman da sakatarorin dindindin da sauran masu rike da mukaman gwamnati da jami’an jam’iyya da sarakunan gargajiya da su sanya ido tare kan yadda ake gudanar da rajistar masu kada kuri’a a fadin jihar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar kwamishinan yada labarai na jihar, Honorabul Magaji Dosara ya bai wa manema labarai a jihar.
A cewar sanarwar, ana sa ran duk wanda ya haura shekaru 18 zai shiga cikin wannan aiki, yana mai cewa hakkinsu ne da kundun tsarin mulki ya ba su na zaben shugabanninsu.
Gwamna Matawalle ya yi kira ga jama’a da su yi rajistan kada kuri’a don kada su koka daga baya
A wnai labarin kuma na daban.
Jam’iyyar NNPP ta ce yanzu haka tattaunawa tayi nisa tsakanin su da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party Peter Obi.
Peter dai yanzu haka shine ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, Kuma shine suke fatan ya zama mataimakin dan takarar su na shugaban kasa wato Rabi’u Musa Kwankwaso.
NNPP ta bayyana hakan ne a yau Asshar, a shafin jam’iyyar ma Twitter, kamar yadda suke fatan kudirin nasu ya tabbata.
Sanarwar ta kara da cewa tuni aka sanya kwamitin mai karfi don kula da batun, kuma shine zai tabbatar da sun samu Peter Onu matsayin mataimakin Kwankwason.
A jiya Juma’a ne dai hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ke cika kan batun mataimakin shugaban kasa ga jam’iyyun siyasar kasar nan.
Yanzu haka dai tuni jam’iyyar PDP ta sanar da gwamnan Delta Eyeanyi Okowa a matsayin mataimakin dan takarar shugaban kasar ta, ita kuma APC ta mika sunan wanda suke fatan ya zama mataimakin dan takarar shugaban kasar su.