Gwamnatin jihar Ribas karkashin jagorancin gwamna Nyesom Wike na kokarin bata sunan Manjo Janar Sharam Jamil G.O.C.6 dake rundunar soja a jihar Fatakwal babban birnin jihar Ribas.
Gwamnan jihar ta Ribas na ikirarin Manjo Janar Sharam Jamil shine shugaban masu fasa Bututun mai a yankin Neja Delta.
Bincikenmu ya gano cewa Manjo Janar Sharam Jamil ba shi da wata alaka ko ta kusa ko ta nesa da masu fasa Bututun mai a jihar ta Ribas, hasali ma al’ummar jihar Ribas sun shedi Manjo Sharam cewa mutumin kirki ne dan kishin cigaban kasa mai goyon bayan ayi gaskiya duba da irin matsalolin dake faruwa a jihar Ribas na fasa Bututun mai da sace-sacen mutane.
Da yake zantawa da Manema Labarai, Manjo Janar Sharam Jamil yace “Ana yunkirin alakanta ni da masu satar mai a yankin Ribas ne domin a bata min suna, duk da kokarin da nake yi wajen matsawa sojoji na don a magance matsalar satar mai a yankin da sauran laifuka.”
“Yin hakan kuma ya biyo baya ne tun daga lokacin da aka bani shugaban sojojin yankin bisa yadda na rike gaskiya da amana kuma nake matsawa ‘yan ta’addan dake fasa Bututun mai a jihar Ribas.” Inji Manjo Sharam Jamil.