By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom, a ranar Alhamis, ya yi Allah wadai da rikicin da ya barke tsakanin al’ummar Tiv da Jukun a bakin kogin Makurdi kan mallakar tafkunan kamun kifi a yankin.
A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan, Nathaniel Ikyur ya fitar, Ortom ya yi kira ga al’ummomin biyu da su daina tashin hankali ba tare da bata lokaci ba.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa an samu raunata mutane biyu da munanan raunuka sakamakon rikicin da ya barke a ranar Larabar da ta gabata, kan yakin neman mallakar tafkunan kamun kifi a yankin Wurukun da ke Makurdi, babban birnin jihar.
An ce basarake na al’ummar ya gudu ne zuwa inda ba a san inda yake ba bayan da matasan da suka afkawa gidan sa suka kona gidaje da dama.
Ortom, wanda ya nuna bakin cikinsa kan rikicin, ya umurci jami’an tsaro da su karbe iko da yankin tare da yin duk abin da ake bukata domin kamo wadanda suka haddasa rikicin.
Ya ce, “Wajibi ne a hukunta wadanda suka haddasa wannan kazamin fadan da ya yi sanadin jikkata da kuma asarar dukiyoyin jama’a. Ba za mu iya jure wa yanayin da mutane ke ɗaukar doka a hannunsu ba.
“Komai yawan fushin da ke cikin zuciyar mutum, neman tashin hankali ba zai zama mafita ba.
Komawa zuwa taimakon kai na iya dagula lamarin. Akwai halaltattun ofisoshin yan sanda da yawa don warware husuma. Kada wani ya dauki doka a hannunsa”.
Ortom ya yi gargadin cewa gwamnatin jihar za ta kawo cikakken nauyin dokar kan duk wani ko al’ummar da ke tada rikici da kuma kawo cikas ga zaman lafiyar kasar nan.
Don haka ya bukaci jama’a da su kasance masu bin doka da oda kamar yadda ya ba su tabbacin cewa gwamnati za ta ci gaba da samar da yanayi mai kyau ga kowa da kowa don gudanar da sana’arsa ta halal a jihar.