Gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya yi ganawar sirri da tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo a garin Abeokuta na Jihar Ogun.
Kakakin tsohon shugaban ƙasar Kehinde Akinyemi ya ce Tambuwal ya ziyarci Obasanjo ne a ranar Asabar domin neman shawarwari a kan al’amuran shugabanci da sauran matsaloli.
Takardar da ya fitar ta ambato gwamnan na cewa Obasanjo, “Shugabanmu ne kuma dattijo, don haka yana da kyau mu ziyartarsa mu gaishe shi tare da duba lafiyarsa sannan mu nemi shawarwari gami da batutuwan shugabanci lokuta-lokuta”.
Ya ce gwamnan ya nuna jin daɗi da ganin Obasanjo cikin ƙoshin lafiya da walwala.
“Za mu ci gada da ɗaukar darasi daga gare shi da kuma ƙwarewa da hikima da tarin iliminsa kan abubuwan shugabanci na wannan zamani”, cewar Tambuwal.
Game da matsalolin jihar Sokoto, Tambuwal ya ce, “Muna ƙoƙarin samar da zaman lafiya a jihohin Arewa inda ake fama da matsalolin ‘yan bindiga.
“Tsaro na samuwa, mutane na komawa gonakinsu da ƙauyukansu daga sansanonin gudun hijira.
“Muna yin iya ƙoƙarinmu a matsayin gwamnatocin jihohi wajen ganin tsaro ya samu da ci gaban al’umma da samuwar ayyuka.