Gwamna Yahaya Bello ya gabatar da kasafin kudi shekarar 2022 Wanda ya Kai Naira 145,896,072,913 ga majalisar dokokin jihar Kogi .
Ya ba da bayyana Naira 90,151,291,251 a matsayin kudaden da za’ayi amfani da su wurin cigaba da sauran ayuka, wanda ya nuna kashi 61.79 kenan cikin 100, da kuma N55,744,781,662 na Manyan aiyukan Wanda ya dauki kashi 38.21 kenan cikin 100.
Gwamnan ya ce kasafin kudin mai taken “Budget of Accelerated Result” an tsara shi ne domin cimma muhimman manufofin tattalin arziki, tare da tabbatar da samar da ingantaccen shugabanci.
Gwamnan ya kara da cewa, za a mayar da hankali wajen kammala dukkan ayyukan da ake gudanarwa, da kuma kara sabbin ayyuka a wuraren da ake bukata, da fadada samar da kudaden shiga ta yadda za a rage dogaro kan rabon kudaden daga Gwamnatin tarayya, da kuma ci gaba da bin bashi mai dorewa ta yadda za a rage martabar basussukan cikin gida na jihar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Hukumar KAROTA ta Kori Jami’an ta Daya, bayan ya Fasa Tayar Babban Mota
Ya kuma ce kasafin kudin zai nemi samar da yanayi mai kyau ga masu zuba jari, da hukumomin bayar da tallafi don gudanar da ayyukansu a jihar, tare da inganta gaskiya da rikon amana da kuma tafiyar da kudaden gwamnati yadda ya kamata.
A wani Labarin Kuma na daban.
Asusun kula da Kananan yara na Majalisar dinkin duniya (UNICEF) ya ce ta kashe dala miliyan 1 domin inganta harkokin kiwon lafiya, da kuma rage mace-macen mata da yara a kananan hukumomi 13 ciki harda karamar hukumar Kwami ta jihar Gombe.
Wakilin UNICEF a Najeriya Mista Peter Hawkins ne ya bayyana hakan a jiya a yayin bikin rufe tallafin ga cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko (PHCs) guda 13 da aka farfado dasu a karkashin wani shiri mai taken ‘Sakamakon Lafiyar Mata, Jarirai da Yara (MNCH)’ a yankin Kwami, na Karamar.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa, daga shafin sadarwa na yanar gizo na North East Trust cewa, sakamakon da aka samu na MNCH wani shiri ne na dala miliyan 1 da gwamnatin kasar Sin ta samar a shekarar 2020 a karkashin asusun ba da taimakon hadin gwiwa na kudu maso kudu na kasar Sin (SSCAF) da nufin inganta lafiyar mata, jarirai da yara baki daya.
An zabi karamar hukumar Kwami ne a jihar Gombe domin cin gajiyar hukumar ta SSCAF, wadda aka kafa ta musamman domin taimakawa kasashe masu tasowa wajen kara kaimi don cimma nasarar shirin na SDG.
Kayayyakin PHC guda 10 da suka amfana a karamar hukumar Kwami sun hada da, Bojude, Daban Fulani, Doho, Dukkkul, Gadam, Jurara, Komfulata, Kwami, Mallam Sidi da Maleri.
Mista Hawkins ya bayyana cewa cibiyoyin sun inganta yanayin kiwon lafiyar mata da yara ta hanyar farfado da tsarin bayar da lafiya a matakin farko, ta yadda za a kawo wuraren rigakafin cutar COVID-19 kusa.
A cewarsa, shirin na hadin gwiwa ne tsakanin gwamnatin jihar Gombe da hukumar UNICEF da gwamnatin kasar Sin.
“Wannan zai taimaka matuka wajen rage mace-macen mata da kananan yara.Kalubalen shi ne a tabbatar da an yi irin wannan gogewa a karamar hukumar Kwami a wasu sassan jihar, wato matakin zuba jari a fannin horar da ma’aikata, don ganin an inganta lafiyar iyaye mata da yara a jihar.”
Mataimakin gwamnan jihar, Dr Manassah Daniel Jatau, ya ce taimakon UNICEF ya taimaka wajen dakile kalubalen da yara ke fuskanta musamman a yankunan karkara.
Comments 1