• About Us
  • Blog
  • Gwamnatin Jihar Kano ta ce ana gabda fara ginin masana’antun Iskar Gas a Jihar
  • Home
Wednesday, October 4, 2023
  • Login
Dimokuradiyya
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
Dimokuradiyya
No Result
View All Result
Home Labarai

Gwamnan Bauchi Da Kwamishinan ‘Yan Sanda Sun Sha Alwashin Magance Matsalar Tsaro

Mustapha Haruna Dabai by Mustapha Haruna Dabai
May 15, 2019
in Labarai
Reading Time: 2 mins read
0 0
0
0
SHARES
4
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Gwamnan jihar Bauchi, Lauya Muhammad A. Abubakar na jam’iyyyar APC, da sabon Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Bauchi, CP Habu Sani Ahmadu sun sha alwashin shawo kan matsaloli da kalubalen tsaro da jihar Bauchi ta ke fuskanta. Sun sha wannan alwashin a tsakaninsu ne a lokacin da kwamishinan ‘yan sandan ya kai ziyara fadar gwamnatin jihar ga gwamna Abubakar a ranar Lahadi. Da ya ke jawabinsa, CP Ahmadu ya shaida cewar tunin ya gana da dukkanin Kwamandojin yanki-yanki da sauran manyan jami’an da suke karkashin shalkwatarsa domin ganin yadda za a yi a inganta tsaro da shawo kan dukkanin matsalolin tsaro da suke fuskantar jihar ta Bauchi. Kamar yadda ya ke shaidawa, cewar jami’an tsaro na ‘yan sanda a jihar sun sake nazarin sabbin daburun aiki da tsare-tsaren daukan matakan da zai basu cikakken damar cin nasarar da suka sanya a gaba. Kwamishinan ya kuma jinjina wa gwamnan jihar Abubakar a bisa hadin kai da goyon bayan da yake baiwa ‘yan sanda a jihar domin su samu zarafin sauke nauyin da ke kansu. Daga bisani ya nemi gwamnatin ta ci gaba da basu cikakken hadin kai domin su samu nasarar gudanar da aiyukan su yadda ya dace. Kwamishina ‘yan sandan  ya baiwa masu zuba jari a jihar musamman ganin cewar yanzu haka aikin hadakar Mai na gudana a jihar tabbacin cewar zaman lafiya da tsaro mai nagarta. Da ya ke maida jawabinsa, gwamnan jihar Bauchi, Muhammad Abubakar ya yi wa sabon Kwamishinan lale da marhaban zuwa jihar, yana mai cewa jihar tana cin gajiyar zaman lafiya mai tsafta a dukkanin fadin jihohin arewa maso gabas, inda ya nuna jihar a matsayin jihar da ta fi kowace jiha samun zaman lafiya a yankin. Ya kuma ce jihar tana ci gaba da morar wannan zaman lafiyar wanda tun lokacin da ya hau kan mulki babu wani rikicin da aka samu aukuwarsa a jihar. Daga bisani ya kirayi ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro da su kara ninka hazakarsu wajen shawo kan ‘yan matsalolin tsaro da suke fuskantar jihar a halin yanzu. “Ina son ku tashi tsaye wajen shawo kan matsalar ’yan Sara-Suka wadanda a sakamakon su an samu asarar dukiyoyin jama’a da dama. Za mu tabbatar da yin duk mai iyuwa wajen ganin an shawo kan wannan matsalar,” Inji gwamnan jihar ta Bauchi.

Previous Post

An Bankado Makarkashiyar Canza Dokokin Majalisar Wakilai Ta Kasa

Next Post

Cikin Sati Daya ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 33 – Matasan Batsari

Next Post

Cikin Sati Daya ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 33 - Matasan Batsari

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result
  • Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    2710 shares
    Share 1084 Tweet 678
  • Batun Dakatar Da Opay Da Palmpay, CBN Ya Bayyana Gaskiyar Zance

    2416 shares
    Share 966 Tweet 604
  • Da Ɗumi-Ɗuminsa: Ƙazamin Rikici Ya Kaure Tsakanin Shugaban Ƙungiyar CAN Da Isa Ashiru Kudan

    2204 shares
    Share 882 Tweet 551
  • Sai na yi lalata da kai na kwanaki 4 babu ƙaƙƙautawa sannan zan taimaka maka, Wata mata ga saurayi

    2091 shares
    Share 836 Tweet 523
  • Ga Irinta Nan: Budurwa Ta Koka Bayan Saurayinta Ya Ƙi Amsar Cikin Da Ya Ɗirka Mata

    1507 shares
    Share 603 Tweet 377
Majalisar Dattijai

Majalisar Dattawa ta fara bincike kan kisan Ƴan Najeriya 250 a Habasha

October 4, 2023
NSCDC

NSCDC ta horar da Ma’aikatan ta 280 Kan Sarrafa Makamai

October 4, 2023
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Naija Ta Fara Tattara Bayanan Masu Haƙar ma’adinai a jihar

Gwamnan Neja ya jajantawa Masarautar Borgu kan hatsarin jirgin ruwa

October 4, 2023
Auto Draft

Saudi Arabiya ta sanar da buƙatar karbar bakuncin gasar cin kofin duniya

October 4, 2023
Bola Tinubu

Jami’ar Jihar Chicago: Takardun Tinubu ba na bogi ba ne ba – Fadar Shugaban Kasa

October 4, 2023
Jamiyyar APC A Wata Jiha Ta Kori Zababben Sanata Da Dan Takarar Gwamna

APC ta Yi Watsi da Hukuncin Kotun Sauraren Kararrakin Zabe

October 4, 2023
Majalisar Dattijai
Labarai

Majalisar Dattawa ta fara bincike kan kisan Ƴan Najeriya 250 a Habasha

October 4, 2023
NSCDC
Labarai

NSCDC ta horar da Ma’aikatan ta 280 Kan Sarrafa Makamai

October 4, 2023
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Naija Ta Fara Tattara Bayanan Masu Haƙar ma’adinai a jihar
Labarai

Gwamnan Neja ya jajantawa Masarautar Borgu kan hatsarin jirgin ruwa

October 4, 2023
Majalisar Dattijai

Majalisar Dattawa ta fara bincike kan kisan Ƴan Najeriya 250 a Habasha

October 4, 2023
NSCDC

NSCDC ta horar da Ma’aikatan ta 280 Kan Sarrafa Makamai

October 4, 2023
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Naija Ta Fara Tattara Bayanan Masu Haƙar ma’adinai a jihar

Gwamnan Neja ya jajantawa Masarautar Borgu kan hatsarin jirgin ruwa

October 4, 2023

Twitter

Archives

Recent Posts

  • Majalisar Dattawa ta fara bincike kan kisan Ƴan Najeriya 250 a Habasha
  • NSCDC ta horar da Ma’aikatan ta 280 Kan Sarrafa Makamai
  • Gwamnan Neja ya jajantawa Masarautar Borgu kan hatsarin jirgin ruwa

Quick Links

  • Tsaro
  • Siyasa
  • Labarai
  • Wasanni
  • Kasuwanci
  • Rikicin Duniya

Contact Us

info@dimokuradiyya.com.ng

0809 912 4425 +234 809 912 4425

No. 218 Mogadishu layout Kaduna City Center Ahmadu Bello way kaduna. Kaduna, Nigeria 800273

Copyright © 2023 Dimokuradiyya Media Services LTD.

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio

Copyright © 2023 Dimokuradiyya Media Services LTD.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In