Gwamna jihar Benue Samuel Ortom ya rattaba hannu kan wasu dokoki guda biyu da suka baiwa bangaren shari’a da ‘yan majalisar dokokin jihar damar cin gashin kansu a fannin tasarrafi da kudi.
Gwamnatin jihar za ta kafa kwamitin rabon kudin jihar don ware kudaden ga bangarorin gwamnati uku, bayan sanya hannu kan dokar.
Kwamishinan shari’a kuma babban lauyan gwamnati, Michael Gusa, ya shaida wa manema labarai jiya Alhamis a Makurdi, cewa daga cikin amfanin dokokin shine kula da kudaden da ake samu daga bangaren shari’a, daga asusun tattara kudaden shiga, yayin da daya kuma zai tabbatar da sarrafa kudaden da suke karba a jihar Benue ga Majalisar dokokin jihar.
Ya kuma an dorawa kwamitin alhakin raba kudaden da ake samu a jihar a duk wata ta hanyar da ta dace da bangarorin gwamnati guda uku.