Gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom, ya bukaci gwamnatin tarayya ta bai wa ’yan Nijeriya izinin mallakar bindiga kirar AK47 don kare kansu daga mahara.
Gwamna Ortom ya yi wannan kiran ne a yayin gabatar da wata takarda a lokacin tattaunawarsa da cibiyar inganta shugabanci (CVL) tare da hadin gwiwar kungiyar gwamnonin Nijeriya.
Taron ya bukaci a yi dokar da za ta bai wa ’yan kasa izinin mallakar makamai da kuma hukunta wadanda suke rike da su babu lasisi kamar yadda jaridar Daily Trust ta labarto.
A takardar da ya gabatar mai taken, ‘Kalubalen tsaro da matsalolin shugabanci a wannan lokaci’, Ortom ya bukaci dukkannin matakan gwamnati su fahimci cewa kalubalen tsaro yana yin cikas ga ci gaban kasa, don haka su tashi su magance ta.
Ya kuma yi kira da a wadatar da hukumomin tsaro da kayan aiki tare da horar da jami’ansu don magance kalubalen tsaro.
Gwamnan ya kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da dokar samar da labin makiyaya don magance rikicin makiyaya da manoma.