Gwamnan Jihar Cross River, Farfesa Ben Ayade, ya cire rawanin Muri Munene na ƙasar Efut kuma babban mai riƙe da sarautar Calabar ta Kudu, Itam Hogan Itam.
An ce ya saɓa wa sashe na 30, ƙaramin sashe na 3 na dokar gargajiya ta jihar Cross River mai lamba 14 na shekarar 1978 sakamakon halartar taron jam’iyyar PDP na mazaɓar Sanata ta Cross River ta kudu inda a ka ce Sarkin ya goyi bayan ɗan takarar gwamna, Arthur Jarvis Archibong.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yanzu Najeriya na hannun Ƴan bindiga, ku biya buƙatar su, don sako wanda aka sace — Sheikh Gumi
An kuma yi zargin cewa shi ma sarkin ya kada kuri’a a taron tare da sanya hannu kan rijistar halartar taron.
Ana zargin wani tsohon gwamnan jihar Donald Duke ne ya jagoranci taron.
Babban Basaraken Karamar Hukumar Bakassi kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta CRS, Etinyin Edet, ya shawarci sarakuna su guji siyasar bangaranci.
Gwamnan ya ba da umarnin karɓe takardar shaidar naɗa sarkin ne a wata wasika da ya aike wa mai martaba Sarkin mai kwanan watan 11 ga Mayu, 2022 mai dauke da sa hannun mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin masarautu, Adoga Victor.