Gwamnan da ya ke faɗa da Buhari, ya gayyace shi Ƙaddamar da mahimman ayyuka a Jihar sa
Gwamnan jihar Benue Samuel Ortom ya yi wa shugaban kasa Muhammadu Buhari wata gayyata mai ban mamaki da ya kaddamar da wasu sabbin gidaje guda biyu da aka gina a gidan gyaran hali na Makurdi da ke jihar.
Gwamna Ortom ya bayyana hakan ne a wani taro da al’ummar Ugondo, mai masaukin baki na ma’aikatan gidan gyaran hali.
KARANTA WANNAN LABARIN: 2023: Ba mu da wani ra’ayi kan wanda zai zama shugaban Najeriya – Birtaniya
Idan dai za a iya tunawa, a baya Gwamna Ortom ya sha sukar gwamnatin shugaba Buhari a karkashin jam’iyyar APC, musamman ma dangane da hare-haren da Fulani makiyaya suka kai a wasu sassan jihar Benue, wanda ya yi sanadin rasa rayuka da lalata dukiyoyi.
Bugu da kari, gayyatar na zuwa ne a daidai lokacin da Ortom ke yaƙi da ‘yan kungiyar ‘Integrity Group’ da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, kan ci gaba da rike Iyorchia Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa.
Kungiyar dai tana son Ayu ya yi murabus ne a matsayin wani sharadi na marawa Atiku baya a zaben shugaban kasa da ke tafe a 2023.
An fara aikin gina sabbin cibiyoyin gyaran gidajen yari ne biyo bayan rahotannin da aka samu na fasa gidajen yari a fadin kasar nan, ciki har da na karamar hukumar Kuje da ke babban birnin tarayya Abuja, da dai sauransu.
Gwamnan ya gargadi al’umma game da yin katsalandan a filin da aka bayar ga ma’aikata da duk wata hukumar tarayya da ke bayar da gudunmawar ci gaban al’ummar Benuwai da kuma tsaron lafiyarsu.
A wani labarin kuma: An Gargaɗi Ƴan Sanda Su Daina Zaluntar Mutane a Kasuwar Alaba
Kungiyar Marubuta Kare Hakkokin Dan Adam ta Najeriya, HURIWA, ta bukaci babban sufeton ‘yan sandan Najeriya Alhaji Usman Alkali Baba ya umurci mataimakinsa sifeto janar na ‘yan sanda (FCID), Mista Johnson Babatunde Kokumo da ya karbi roko da wani dan asalin kasar Madumere Ugochukwu ya shigar da kara akan kasuwar Alaba Legas da ya ke gudanar da kasuwancinsa a karkashin kamfanin Nigrshine Industry Limited wanda ya shigar da karar wasu ‘yan China biyu Gaoxi Ong da Chen Xiao Ming.
HURIWA ta ce wasu sahihan jami’an kotuna da ke Abuja sun sanar da cewa wani alkalin babbar kotun tarayya mai shari’a Taiwo Taiwo mai ritaya ya bayar da umarnin kwace wasu kananan kayayyakin da ake zargin ‘yan kasar China ne suka shigo da su Najeriya, wanda aka ce sun saba wa doka.