Gwamnan Jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu ya amince da fitar da kudi Naira biliyan biyu da miliyan dari tara da goma sha takwas da dubu dari takwas da hamsin da shida , da dari hudu da sittin da biyar da kobo ar’ ba’in da takwas, (N2,981,856,465.48) domin biyan kudade ma ‘aikan da suka ajiye aiki da wadanda suka rasa rayuknsau a shekarar 2021.
Ana sa ran kudade sun kunshi kudade jin dadi ma’ aikata a matakin kananan hukumomi da jiha , wanda adadin su ya kai dubu daya da dari daya da saba’in da biyu .
Wannan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a jiya Talata , dauke da sa hannu Mai rike da mukamin Shugaban Maaikata na jihar Kebbi Safiyanu Garba Bena.
Sanarwar ta kara da cewa umurnin gwamnan yana daga cikin kudirin gwamnati mai ci na tabbatar da biyan Ma’aikan da suka ajiye aikinsu hakokinsu a cikin lokacin da ya dace.
Idan dai za a iya tunawa Gwamna Bagudu , ya bayar da umurnin fitar da Naira Biliyan 30.2 domin biyan hakokin ma’aikatan da suka ajiye aiki a shekarar 2015 zuwa 2018, da kuma na 2019 zuwa 2021.
Izuwa yanzu Bayanai sun tabbatar da cewa akalla wadanda suka aniye aiki dubu uku da dari bakwai da ashirin da hudu (3,724) ne suka amfana da hakkokin su na ajiye aiki Karkashin gwamnati mai ci.
Comments 1