Darakta Janar na Yada Labarai ga gwamna Abdullahi Bego a wata sanarwa, ya ce shugaban sa zai dawo Najeriya ranar 14 ga watan Agusta.
A cewar Bego, ‘yan majalisar wakilai biyu daga jihar, Lawan Shettima Ali da Tijjani Zanna Zakariya da kuma Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin jihar, Muhammad Auwal Isa da kuma Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar, Mohammed Gadaka, sun yi tafiya tare da gwamnan don aikin hajji.