Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle ya tabbatar da harin da aka kai wasu al’ummomi a kananan hukumomin Bukuyyum da Anka.
Sama da mutane 60 ne aka kashe duk da cewa babu wata kididdigar da aka samu daga gwamnati ko hukumomin tsaro.
Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a kauyuka biyar a kananan hukumomin Bukuyyum da Anka a daren Laraba
Al’ummar su ne Kurfa Danya, Kurfa Magaji, Rafin Gero, Tungar Isa da Barayar Zaki a kananan hukumomin Bukkuyum da Anka.
Gwamnan ya tabbatar da hakan ne a wani sansanin sojoji da aka yi a Gusau a lokacin da ya ziyarci masu raunuka jihar Zamfara na 82 na rundunar sojojin Najeriya.
Ya kuma yabawa gwamnatin tarayya bisa ayyana ‘yan bindiga a matsayin ‘yan ta’adda
Mista Matawalle ya lura cewa a yanzu haka sojoji za su iya fatattakar ‘yan bindiga a yankunansu
Gwamnan Zamfara ya nemi a tura jirgin Tucano zuwa dazukan Zamfara.
Dukkanin Al’ummomin da ke cikin tashin hankali a cewarsa nan ba da dadewa ba za su sami kubuta daga ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.