Gwnamnan Jihar Kebbi Alhaji Atiku Abubakar Bagudu ya ce zai shiga daji tare da mafarauta don ceto ɗaliban da aka sace na makarantar sakandaren Birnin Yauri dake karamar hukumar Ngaski ta Jihar.
Bagudu wannda shine Shugaban Ƙungiyar ci gaban gwamnoni ya yi wannan ikirari ne yayin da maharban jihar suka kai masa ziyara.
Kazalika kamfanin dillancin labarai na Kasa NAN ya labarto cewa, baya ga kungiyar maharban ita ma ƙungiyar gwamnonin Najeriya karkashin shugabanta Kayode Fayemi kuma Gwamnan Jihar Ekiti ta kai wa Gwamnan ziyarar jajantawa.
Bagudu ya tabbatar da cewa ba shi kaɗai ba, karin wasu gwamnonin za su rufa mishi baya wajen dunguma zuwa daji don ceto daliban.
Ya kara da cewa ba kuma za su yi hakan ne gaba gaɗi ba, sai sun tattauna da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki don gudun kawo katsalandan ga harkar ceto ɗaliban.
Ya ce “Toh, kamar yadda na alkawarta muku, za mu fito mu dunguma zuwa dajin tare, kuma ranar da za a tafi ba zan je ofis ba”
Bagudu ya bayyana cewa indai dubban jama’a za su fito su ui gangami yayin yakin neman zabe, to bai ga dalilin da zai sa su ma a saka musu ba a daidai wannan lokaci.
Comments 1