By Abbas Yakubu Yaura
A jiya ne gwamnatin jihar Gombe tace ta dakatar da kiwon da kananan yara da makiyaya ke yi a ciki da wajen jihar na tsawon watanni uku.
Kwamishinan yada labarai da al’adu na jihar, Mista Julius Ishaya Lepes ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan sakamakon taron tsaron jihar da gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya kira.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa gwamnatin ta kuma umurci manoman jihar da su girbe amfanin gonakinsu a cikin watanni uku da aka kayyade, inda yace an dauki matakin ne domin kaucewa rikicin manoma da makiyaya a jihar.
A cewarsa, kudurorin majalisar sun nuna cewa ba za a yi noma da kiwo daga karfe 6 na yamma zuwa 6 na safe ba.
“Ba a barin manoma su kona dabbobinsu, a cikin sauran gonakinsu.Hakan ne don tabbatar da cewa idan an gama girbinsu, makiyaya za su iya shiga su amfana da ragowar abincin dake cikin gonakin.
“Majalisar ta kuma ba da umarnin cewa ba za a bar makiyaya da shanun su shiga ko kuma fita daga jihar Gombe ba har sai an girbe amfanin gona wanda zai kai har karshen watan Janairun 2022,” in ji kwamishinan.