Gwamnatin tarayya ta gargadi iyayen yara akan tura ‘ya’yansu zuwa jami’o’i a Arewacin Cyprus sakamakon kashe-kashen dalibai ‘yan Nijeriya da ake yi.
Abike Dabiri-Erewa, shugabar hukumar lura da ‘yan Nijeriya a kasashen waje, NIDCOM, ita ce ta yi wannan gargadin a yayin da ta karbi tawagar da Amina Bello, Alkaliya wacce take mahaifiya ce ga Ibrahim Khaleel, wani dalibin Nijeriya da aka yi zargin an kashe shi a Cyprus.
Ta kara da cewa mutuwar Khaleel, wanda yake dalibi ne a bangaren Injiniya, yana daga cikin wadanda ya rasa ransa sakamakon kashe dalibai ‘yan Nijeriya da ake yi a kasar.
Shugabar NIDCOM, ta bayyana sunayen dalibai ‘yan Nijeriya 15 da aka kashe cikin fiye da 100 a kasar, ta ce yana da matukar wahala a yi tattaunawar diflomasiyya domin binciken abubuwan da suka faru a kasar, domin kasar Turkiyya ne kawai daukar Cyprus a matsayin kasa.
“Kashe Ibrahim Khaleel ya kamata ya zama madakata ta karshe na kashe mana ‘ya’yanmu a fadin duniya musamman ma a Arewacin Cyprus.” Inji ta.
“Ba kawai Ibrahim aka kashe ba, an kashe Kennedy Dede 28, Augustine Ngok, Gabriel Sorewei, Osabanjo Owoyale, Augustine Wallace, Stanley Eteno, Hassan Babatunde, Temitayo Adigun, da Kubat Abraham da wadansu ma da muka sani.” Ta tabbatar.
Ta tabbatar da cewa matsalar iyayen Nijeriya ba su san cewa Cyprus ba kasa ba ce, majalisar dinkin duniya ma ba ta san da ita ba.