Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa za ta yiwa kafafen sada zumunta garambawul. Inda ta ce shafukan sada zumunta a yau, ana amfani da shi ba bisa ka’ida ba.
Lai Mohammed, Ministan yada labarai da al’adu, shi ne ya bayyana hakan a taron menama labarai a birnin tarayya Abuja a ranar Talata.
Lai Mohammed ya ce; gwamnati tana duba yadda za a ta tsaftace yadda za a rika amfani da shafukan sada zumunta. Domin a cewarsa, yanzu shafukan sada zumunta ya zama babban barazana ga hadin kan kasarnan. Inda ya ce Nijeriya ba ita ce kasa ta farko da ta tsaftace amfani da shafukan sada zumunta ba, inda ya tabbatar da cewa; abubuwan da yake gudana a wadannan shafukan, gwamnati ba za ta yarda da su ba.