Gwamnan Jihar Kuros Riba, Ben Ayade, ya amince da sake fasalin albashi da kuma jin dadin jami’an shari’a a jihar.
Ya sanar da sabon kunshin albashin ne a zauren zartarwa na ofishin gwamna, a Calabar.
Sabon kunshin albashin zai fara aiki ne daga ranar 1 ga Agusta, 2022, kuma za a kara albashin alkalan babbar kotun jihar da kashi 100 cikin 100.
An kuma bayyana cewa alkalan kotun daukaka kara na gargajiya za a kara musu albashi da kashi 100, yayin da na Kotun Majistare za a kara musu kashi 50 cikin 100.
Hakazalika, gwamnan ya baiwa dukkan jami’an shari’a na jihar rabon fili nan take.
Ya kuma amincewa Babban Alkali tare da goyon bayan Shugaban Ma’aikata da Hukumar Kula da Ma’aikata, a dauki ma’aikata 500 a ma’aikatar Shari’a a matakin farko kadai.
A cewarsa, gwamnatinsa ta amince da ware kashi 25 cikin 100 na manyan kudade don tallafawa alawus-alawus na jami’an shari’a ta fuskar hutu, tafiye-tafiye da dai sauransu.
Ya ce ya magance kalubalen da ke addabar bangaren shari’a na jihar, ya kuma yi alkawarin tallafa wa wannan bangaren na gwamnati.
Ya ce ya yi aiki ne bisa rahoton kwamitin kula da jin dadin shari’a na jihar da ya kafa a watan Afrilu. Kwamitin ya kori mai shari’a Eyo Effiong Ita a matsayin shugaba da shugaban ma’aikata na jihar, Timothy Ogbang Akwaji a matsayin sakatare.