Daga: Abbas Yakubu Yaura
Gwamnatin jihar Gombe ta sake bude kwalejojin fasahar kiwon lafiya masu zaman kansu guda 5 daga cikin 27 da ta rufe a baya-bayan nan saboda rashin basu izinin gudanar da ayyukan shirye-shiryen kiwon lafiya a jihar.
Kwamishinan lafiya na jihar Dr Habu Dahiru ne ya bayyana hakan a wata hira da yayi da manema labarai jiya a Gombe.
KARANTA WANNAN LABARIN: https://dimokuradiyya.com.ng/sakatare-janar-mai-jiran-gado-na-opec-ya-yi-taaziyyar-mutuwar-magabacinsa-barkindo/
Ya ce gwamnatin jihar ta kaddamar da wani kwamiti da zai duba yadda ake samun yawaitar kwalejojin fasahar kiwon lafiya da ke aiki ba tare da lasisi ba.
A cewarsa, a lokacin da za a kafa makarantar kiwon lafiya, akwai ka’idoji da ya kamata a bi su kafin a amince da ita ya kara da cewa akwai bukatar cibiyoyi masu inganci su gudanar da shirye-shiryen kiwon lafiya.
“Don haka idan muka samu rahotanni da korafe-korafe daga jama’a, gwamnati ta rufe dukkan makarantu 27 har sai an kammala binciken kwamitin a kansu,” inji shi.
Kwamishinan wanda ke rike da mukamin shugaban kwamitin ya bayyana cewa, abubuwan da kwamitin ya tanada sun hada da yanayin rajista, samun isassun ma’aikata, dakunan gwaje-gwaje, dakunan karatu da kayan aiki, isassun ajujuwa da asibitin nunawa da dai sauransu.
“A halin yanzu mun sami damar samun kusan biyar wadanda suka cancanta kuma mun riga mun nemi su ci gaba da ayyukan su.
“Mun ziyarci makarantun a wasu al’ummomi kamar Filiya, Bambam, Cham, Kumo, Billiri da Dukku, za mu zagaya zuwa sauran makarantun Gombe da sauran al’ummomin da ke kewaye da su,” inji shi.