By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnatin jihar Gombe ta yabawa mahukuntan Kamfanin (EEC) bisa kammala aikin titin Degri- Bembelem-Reme-Dong-Talasse dake jihar a kan lokaci.
Yabon da gwamnatin jihar ta yi ya fito ne a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Abuja mai dauke da sa hannun Daraktan mai kula da manyan hanyoyin jihar Gombe, Injiniya Aliyu Isa Shinga.
Injiniya Shinga yace aikin hanyar tare da kwangila mai lamba, FGPC / GME / 2019/185 an ba hukumar Kamfanin na EEC ne a cikin watan Oktoba na shekarar 2019 tare da kammala aiki cikin watanni 24.
Yace hanyar data hada al’ummomi da dama a karamar hukumar na da tsawon kilomita 21 wanda take da fadin mita 10.3, wanda ya kunshi magudanan ruwan siminti da dama.
Shinga ya yabawa kamfanin bisa kammala aikin a kan lokaci, yana mai cewa hanyar ta cika dukkan ka’idojin da ake bukata na aminci da inganci.Sannan yace, “Bayan duba aikin da muka yi tare da hadin gwiwa a wurin, kuma bisa ga sashi na 48 na ka’idar kwangilar, an bada shaidar cewa an kammala aikin titin Degri-Bembelem-Reme-Talasse a karshe.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa an kuma ba kamfanin kwangilar kula da shi wanda zai dauki tsawon watanni 12 wanda ya fara a watan Yuni shekarar 2021.Titin wanda ya lashe tsabar kudi kimanin Naira biliyan 3.7 mai tsawon kilomita 21 Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya kaddamar da shi a watan Disamba na shekarar 2019 domin bude yankin da bunkasa tattalin arzikin su.
Gwamnan wanda ya bayyana mahimmancin hanyar, yace idan aka kammala aikin zai hade yankunan kudanci da arewacin karamar hukumar Balanga tare da bude kofa ga jama’a da dama dake kewayen tuddan da kuma bunkasa harkokin noman su.
Comments 1