Gwamnatin jihar Gombe ranar Laraba ta ce ta fara aiki kan hanyoyin da ta ware naira biliyan 13.3 don yin su, wanda a cewar gwamnatin hakan zai saukake sufuri a cikin jihar.
Kwamishinan watsa labarai na jihar, Ibrahim Alhassan, ne ya bayyana haka jim kadan bayan kammala zaman majalisar masu zartaswa na jihar a garin Gombe.
Alhassan ya ce majalisar ta saki kudaden ayyukan hanyoyin da za a yi a cikin jihar.
Ya kara da cewa, yanzu haka ana ayyuka daban-daban a cikin kananan hukumomi 10 na cikin jihar cikin 11.
Kwamishinan ya lissafo wasu kananan hukumomi kamar Balanga, Akko da Kwami, inda ya ce ba a fara aiki a Nafada ba.