Gwamnatin Jahar Kwara Zata Gina Katafaren Asibitin Maganin Ciwon Daji
Gwamanatin Jihar Kwara ta fidda sanarwar yunkurinta na gina katafaren Asibitin maganin ciwon daji wanda za’a yishi cikin babban asibiti dake Ilorin.
Alhaji Bashir Adingu mai ba gwamna shawara ta fannin siyasa ya bayyana haka.
KARANTA:-Mutanen Garin Lafiya na Tafiyar kilomita 200 don Zuwa Babban Asibiti
Kamar yadda ya ayyana Kungiyar Abdul Samad Rabi’u ta baiwa Jahar Kwara tallafi kudi kimanin Biliyan biyu da rabi, yace wannan ba karamin kayayyakin zamani za’a saya dasu ba.
Gwamanan yace a baya kadan sun kawo manyan gadaje guda sha biyu da kuma fannin kula da masu matsalar Ido da Hakori aka kawo a asibitin wanda wannan ba karamin aiki bane wanda gwamnatin tayi.
Yace wannan zai maida asibitin ya zama babban asibitin Koyarwa wanda domin yin anfani da babbar Jami’a dake jahar Kwara.
Yace kuma wannan zai rage makudan kudaden da Mutanen ke kashewa wajan zuwa kashashen waje don magance matsalar cutar daji.
Yace wurin zai zama mai bada taimakon ga Mutanen Kwara da sauran makwaftan jahohi kamar su Neja, Kogi da Osun.
Yace kayayyaki da za’a zuba sune mafiya kyau wajan magance cutar daji, sannan wannan zai sa asibitin ya zama babu kamar sa ya yankin.
Gwamanan yace bayan wannan gwamnatin tana matukar kokari wajan kula da shaanin tsaron Jahar da Kare lafiya da kayayyakin jama’a. Sannan yace jama’a dasu gane shi shaanin tsaro nada bukatar hadin kan kowane mutum a cikin al’umma.